Hausa
Surah Ya-seen - Aya count 83
يس
( 1 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 1 Ya-seen - Aya 1](style/islamic/icons/mp3.png)
Y. S̃.
وَالْقُرْآنِ الْحَكِيمِ
( 2 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 2 Ya-seen - Aya 2](style/islamic/icons/mp3.png)
Inã rantsuwa da Al-ƙur'ãni Mai hikima.
إِنَّكَ لَمِنَ الْمُرْسَلِينَ
( 3 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 3 Ya-seen - Aya 3](style/islamic/icons/mp3.png)
Lalle kai, haƙĩƙa kanã cikinManzanni.
عَلَىٰ صِرَاطٍ مُّسْتَقِيمٍ
( 4 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 4 Ya-seen - Aya 4](style/islamic/icons/mp3.png)
A kan hanya madaidaiciya.
تَنزِيلَ الْعَزِيزِ الرَّحِيمِ
( 5 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 5 Ya-seen - Aya 5](style/islamic/icons/mp3.png)
(Allah Ya saukar da Al-kur'ãni) saukarwar Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
لِتُنذِرَ قَوْمًا مَّا أُنذِرَ آبَاؤُهُمْ فَهُمْ غَافِلُونَ
( 6 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 6 Ya-seen - Aya 6](style/islamic/icons/mp3.png)
Dõmin ka yi gargaɗi ga waɗansu mutãne da ba a yi gargaɗi ga ubanninsu ba, sabõda haka sũmasu rafkana ne.
لَقَدْ حَقَّ الْقَوْلُ عَلَىٰ أَكْثَرِهِمْ فَهُمْ لَا يُؤْمِنُونَ
( 7 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 7 Ya-seen - Aya 7](style/islamic/icons/mp3.png)
Lalle, haƙĩƙa, kalma tã wajaba a kan mafi yawansu, dõmin sũ, bã zã su yi ĩmãni ba.
إِنَّا جَعَلْنَا فِي أَعْنَاقِهِمْ أَغْلَالًا فَهِيَ إِلَى الْأَذْقَانِ فَهُم مُّقْمَحُونَ
( 8 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 8 Ya-seen - Aya 8](style/islamic/icons/mp3.png)
Lalle Mũ, Mun sanya ƙuƙumma a cikin wuyõyinsu, sa'an nan sũ (ƙuƙumman sun kai) har zuwa ga haɓõɓinsu, sabõda haka, sũ banƙararru ne.
وَجَعَلْنَا مِن بَيْنِ أَيْدِيهِمْ سَدًّا وَمِنْ خَلْفِهِمْ سَدًّا فَأَغْشَيْنَاهُمْ فَهُمْ لَا يُبْصِرُونَ
( 9 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 9 Ya-seen - Aya 9](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma Muka sanya wata tõshiya a gaba gare su, da wata tõshiya a bãyansu, sabõda haka Muka rufe su, sai suka zama bã su gani.
وَسَوَاءٌ عَلَيْهِمْ أَأَنذَرْتَهُمْ أَمْ لَمْ تُنذِرْهُمْ لَا يُؤْمِنُونَ
( 10 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 10 Ya-seen - Aya 10](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma daidai yake a gare su, shin, ka yi musu gargaɗi kõ ba ka yi musu gargaɗi ba, sũ bã zã su yi ĩmãni ba.
إِنَّمَا تُنذِرُ مَنِ اتَّبَعَ الذِّكْرَ وَخَشِيَ الرَّحْمَٰنَ بِالْغَيْبِ ۖ فَبَشِّرْهُ بِمَغْفِرَةٍ وَأَجْرٍ كَرِيمٍ
( 11 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 11 Ya-seen - Aya 11](style/islamic/icons/mp3.png)
Kanã yin gargaɗi kawai ga wanda ya bi Alƙur'ãni ne, kuma ya ji tsõron mai rahama a fake. To, ka yi masa bushãra da gãfara da wani sakamako na karimci.
إِنَّا نَحْنُ نُحْيِي الْمَوْتَىٰ وَنَكْتُبُ مَا قَدَّمُوا وَآثَارَهُمْ ۚ وَكُلَّ شَيْءٍ أَحْصَيْنَاهُ فِي إِمَامٍ مُّبِينٍ
( 12 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 12 Ya-seen - Aya 12](style/islamic/icons/mp3.png)
Lalle Mũ, Mũ ne ke rãyar da matattu kuma Mu rubũta abin da suka gabãtar, da gurãbunsu, kuma kõwane abu Mun ƙididdige shi, a cikin babban Littãfi Mabayyani.
وَاضْرِبْ لَهُم مَّثَلًا أَصْحَابَ الْقَرْيَةِ إِذْ جَاءَهَا الْمُرْسَلُونَ
( 13 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 13 Ya-seen - Aya 13](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma ka buga musu misãli: Waɗansu ma'abũta alƙarya, a lõkacin da Manzanni suka jẽ mata.
إِذْ أَرْسَلْنَا إِلَيْهِمُ اثْنَيْنِ فَكَذَّبُوهُمَا فَعَزَّزْنَا بِثَالِثٍ فَقَالُوا إِنَّا إِلَيْكُم مُّرْسَلُونَ
( 14 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 14 Ya-seen - Aya 14](style/islamic/icons/mp3.png)
A lõkacin da Muka aika (Manzannin) biyu zuwa gare su, sai suka ƙaryata su, sa'an nan Muka ƙarfafa (su) da na uku, sai suka ce: "Lalle mũ, Manzanni ne zuwa gare ku."
قَالُوا مَا أَنتُمْ إِلَّا بَشَرٌ مِّثْلُنَا وَمَا أَنزَلَ الرَّحْمَٰنُ مِن شَيْءٍ إِنْ أَنتُمْ إِلَّا تَكْذِبُونَ
( 15 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 15 Ya-seen - Aya 15](style/islamic/icons/mp3.png)
Suka ce: "Kũ ba ku zamo bafãce mutãne ne kamarmu kuma Mai rahama bai saukar da kõme ba, ba ku zamo ba fãce ƙarya kuke yi."
قَالُوا رَبُّنَا يَعْلَمُ إِنَّا إِلَيْكُمْ لَمُرْسَلُونَ
( 16 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 16 Ya-seen - Aya 16](style/islamic/icons/mp3.png)
Suka ce: "Ubangijinmu Yã sani, lalle mũ, haƙiƙa Manzanni nezuwa gare ku."
وَمَا عَلَيْنَا إِلَّا الْبَلَاغُ الْمُبِينُ
( 17 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 17 Ya-seen - Aya 17](style/islamic/icons/mp3.png)
"Kuma bãbu abin da ke kanmu, fãce iyar da manzanci bayyananne."
قَالُوا إِنَّا تَطَيَّرْنَا بِكُمْ ۖ لَئِن لَّمْ تَنتَهُوا لَنَرْجُمَنَّكُمْ وَلَيَمَسَّنَّكُم مِّنَّا عَذَابٌ أَلِيمٌ
( 18 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 18 Ya-seen - Aya 18](style/islamic/icons/mp3.png)
Suka ce: "Lalle mũ munã shu'umci da ku! Haƙĩƙa idan ba ku, hanu ba, haƙĩƙa, zã mu jẽfe ku, kuma haƙĩƙa wata azãba mai raɗaɗi daga gare mu zã ta shãfe ku."
قَالُوا طَائِرُكُم مَّعَكُمْ ۚ أَئِن ذُكِّرْتُم ۚ بَلْ أَنتُمْ قَوْمٌ مُّسْرِفُونَ
( 19 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 19 Ya-seen - Aya 19](style/islamic/icons/mp3.png)
Suka ce: "Shu'umcinku, yanã tãre da ku. Ashe, dõmin an tunãtar da ku? Ã'a, kũ dai mutãne ne mãsu ƙẽtare haddi."
وَجَاءَ مِنْ أَقْصَى الْمَدِينَةِ رَجُلٌ يَسْعَىٰ قَالَ يَا قَوْمِ اتَّبِعُوا الْمُرْسَلِينَ
( 20 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 20 Ya-seen - Aya 20](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma wani mutum daga mafi nĩsan birnin ya je, yanã tafiya da gaggãwa, ya ce: "Ya mutãnẽna! Ku bi Manzannin nan.
اتَّبِعُوا مَن لَّا يَسْأَلُكُمْ أَجْرًا وَهُم مُّهْتَدُونَ
( 21 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 21 Ya-seen - Aya 21](style/islamic/icons/mp3.png)
"Ku bi waɗanda bã su tambayar ku wata ijãra kuma sũ shiryayyu ne."
وَمَا لِيَ لَا أَعْبُدُ الَّذِي فَطَرَنِي وَإِلَيْهِ تُرْجَعُونَ
( 22 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 22 Ya-seen - Aya 22](style/islamic/icons/mp3.png)
"Kuma mene ne a gare ni, bã zan bauta wa Wanda Ya ƙãga halittata ba, kuma zuwa gare Shi ake mayar da ku?"
أَأَتَّخِذُ مِن دُونِهِ آلِهَةً إِن يُرِدْنِ الرَّحْمَٰنُ بِضُرٍّ لَّا تُغْنِ عَنِّي شَفَاعَتُهُمْ شَيْئًا وَلَا يُنقِذُونِ
( 23 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 23 Ya-seen - Aya 23](style/islamic/icons/mp3.png)
"Shin, zan riƙi waninSa abũbuwan bautãwa? Idan Mai rahama Ya nufe ni da wata cũta, to cẽtonsu bã ya amfanĩna da kõme, kuma bã za su iya tsãmar da ni bã."
إِنِّي إِذًا لَّفِي ضَلَالٍ مُّبِينٍ
( 24 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 24 Ya-seen - Aya 24](style/islamic/icons/mp3.png)
"Lalle nĩ, a lõkacin nan, tabbas, inã a cikin ɓata bayyananna."
إِنِّي آمَنتُ بِرَبِّكُمْ فَاسْمَعُونِ
( 25 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 25 Ya-seen - Aya 25](style/islamic/icons/mp3.png)
"Lalle ni, nã yi ĩmãni da Ubangijinku, sabõda haka ku saurãre ni."
قِيلَ ادْخُلِ الْجَنَّةَ ۖ قَالَ يَا لَيْتَ قَوْمِي يَعْلَمُونَ
( 26 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 26 Ya-seen - Aya 26](style/islamic/icons/mp3.png)
Aka ce (masa), "Ka shiga Aljanna." Ya ce, "Dã dai a ce mutãnẽna sunã iya sani."
بِمَا غَفَرَ لِي رَبِّي وَجَعَلَنِي مِنَ الْمُكْرَمِينَ
( 27 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 27 Ya-seen - Aya 27](style/islamic/icons/mp3.png)
"Game da gãfarar da Ubangijjĩna ya yi mini, kuma Ya sanya ni a cikin waɗanda aka girmama."
وَمَا أَنزَلْنَا عَلَىٰ قَوْمِهِ مِن بَعْدِهِ مِن جُندٍ مِّنَ السَّمَاءِ وَمَا كُنَّا مُنزِلِينَ
( 28 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 28 Ya-seen - Aya 28](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma ba Mu saukar da waɗansu runduna ba daga sama a kan (halaka) mutãnensa, daga bãyansa, kuma bã zã Mu kasance. Mãsu saukarwa ba.
إِن كَانَتْ إِلَّا صَيْحَةً وَاحِدَةً فَإِذَا هُمْ خَامِدُونَ
( 29 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 29 Ya-seen - Aya 29](style/islamic/icons/mp3.png)
Ba ta kasance ba face tsawa guda, sa'an nan sai gã su sõmammu.
يَا حَسْرَةً عَلَى الْعِبَادِ ۚ مَا يَأْتِيهِم مِّن رَّسُولٍ إِلَّا كَانُوا بِهِ يَسْتَهْزِئُونَ
( 30 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 30 Ya-seen - Aya 30](style/islamic/icons/mp3.png)
Yã nadãma a kan bãyĩNa! Wani Manzo bã ya zuwa gare su fãce sun kasance sunã mãsu yi masa izgili.
أَلَمْ يَرَوْا كَمْ أَهْلَكْنَا قَبْلَهُم مِّنَ الْقُرُونِ أَنَّهُمْ إِلَيْهِمْ لَا يَرْجِعُونَ
( 31 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 31 Ya-seen - Aya 31](style/islamic/icons/mp3.png)
Ba su gani ba, da yawa Muka halakar da (mutãnen) ƙarnõni a gabãninsu kuma cẽwa su bã zã su kõmo ba?
وَإِن كُلٌّ لَّمَّا جَمِيعٌ لَّدَيْنَا مُحْضَرُونَ
( 32 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 32 Ya-seen - Aya 32](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma lalle bãbu kõwa fãce waɗanda ake halartarwa ne a wurinMu.
وَآيَةٌ لَّهُمُ الْأَرْضُ الْمَيْتَةُ أَحْيَيْنَاهَا وَأَخْرَجْنَا مِنْهَا حَبًّا فَمِنْهُ يَأْكُلُونَ
( 33 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 33 Ya-seen - Aya 33](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma ãyã ce a gare su: ¡asã matacciya, Mu rãyar da ita, Mu fitar da ƙwãya daga gare ta, sai gã shi daga gare ta suke ci.
وَجَعَلْنَا فِيهَا جَنَّاتٍ مِّن نَّخِيلٍ وَأَعْنَابٍ وَفَجَّرْنَا فِيهَا مِنَ الْعُيُونِ
( 34 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 34 Ya-seen - Aya 34](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma Muka sanya, a cikinta (ƙasã), waɗansu gõnaki na dabĩno da inabõbi, kuma Muka ɓuɓɓugar da ruwa daga marẽmari a cikinta.
لِيَأْكُلُوا مِن ثَمَرِهِ وَمَا عَمِلَتْهُ أَيْدِيهِمْ ۖ أَفَلَا يَشْكُرُونَ
( 35 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 35 Ya-seen - Aya 35](style/islamic/icons/mp3.png)
Dõmin su ci 'ya'yan itãcensa, alhãli kuwa hannãyensu ba su aikata shi ba. Shin, to, bã zã su gõdẽ ba?
سُبْحَانَ الَّذِي خَلَقَ الْأَزْوَاجَ كُلَّهَا مِمَّا تُنبِتُ الْأَرْضُ وَمِنْ أَنفُسِهِمْ وَمِمَّا لَا يَعْلَمُونَ
( 36 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 36 Ya-seen - Aya 36](style/islamic/icons/mp3.png)
Tsarki ya tabbata ga Wanda Ya halitta nau'uka, namiji da mace, dukansu, daga abin da ƙasã ke tsirarwa, kuma daga kansu, kuma daga abin da ba su sani ba.
وَآيَةٌ لَّهُمُ اللَّيْلُ نَسْلَخُ مِنْهُ النَّهَارَ فَإِذَا هُم مُّظْلِمُونَ
( 37 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 37 Ya-seen - Aya 37](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma ãyã ce a gare su: Dare Muna feɗe rãna daga gare shi, sai gã su sunã mãsu shiga duhu.
وَالشَّمْسُ تَجْرِي لِمُسْتَقَرٍّ لَّهَا ۚ ذَٰلِكَ تَقْدِيرُ الْعَزِيزِ الْعَلِيمِ
( 38 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 38 Ya-seen - Aya 38](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma rãnã tanã gudãna zuwa ga wani matabbaci nãta. Wannan ƙaddarãwar Mabuwãyi ne, Masani.
وَالْقَمَرَ قَدَّرْنَاهُ مَنَازِلَ حَتَّىٰ عَادَ كَالْعُرْجُونِ الْقَدِيمِ
( 39 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 39 Ya-seen - Aya 39](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma da watã Mun ƙaddara masa manzilõli, har ya kõma kamar tsumagiyar murlin dabĩno wadda ta tsũfa.
لَا الشَّمْسُ يَنبَغِي لَهَا أَن تُدْرِكَ الْقَمَرَ وَلَا اللَّيْلُ سَابِقُ النَّهَارِ ۚ وَكُلٌّ فِي فَلَكٍ يَسْبَحُونَ
( 40 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 40 Ya-seen - Aya 40](style/islamic/icons/mp3.png)
Rãnã bã ya kamãta a gare ta, ta riski watã. Kuma dare bã ya kamãta a gare shi ya zama mai tsẽre wa yini, kuma dukansua cikin sarari guda suke yin iyo.
وَآيَةٌ لَّهُمْ أَنَّا حَمَلْنَا ذُرِّيَّتَهُمْ فِي الْفُلْكِ الْمَشْحُونِ
( 41 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 41 Ya-seen - Aya 41](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma ãyã ce a gare su. Lalle Mũ, Mun ɗauki zuriyarsu a cikin jirgin, wanda aka yi wa lõdi.
وَخَلَقْنَا لَهُم مِّن مِّثْلِهِ مَا يَرْكَبُونَ
( 42 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 42 Ya-seen - Aya 42](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma Muka halitta musu, daga irinsa, abin da suke hawa.
وَإِن نَّشَأْ نُغْرِقْهُمْ فَلَا صَرِيخَ لَهُمْ وَلَا هُمْ يُنقَذُونَ
( 43 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 43 Ya-seen - Aya 43](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma idan Mun so, zã Mu nutsar da su, har bãbu kururuwar neman ãgaji, a gare su, kuma ba su zama anã tsirar da su ba.
إِلَّا رَحْمَةً مِّنَّا وَمَتَاعًا إِلَىٰ حِينٍ
( 44 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 44 Ya-seen - Aya 44](style/islamic/icons/mp3.png)
Sai fa bisa ga wata rahama daga gare Mu, da jiyarwa dãɗi zuwa ga wani ɗan lõkaci.
وَإِذَا قِيلَ لَهُمُ اتَّقُوا مَا بَيْنَ أَيْدِيكُمْ وَمَا خَلْفَكُمْ لَعَلَّكُمْ تُرْحَمُونَ
( 45 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 45 Ya-seen - Aya 45](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma idan aka ce musu, "Ku kãre abin da ke a gaba gare ku da abin da yake a bãyanku, dõmin tsammãninku a ji tausayinku."
وَمَا تَأْتِيهِم مِّنْ آيَةٍ مِّنْ آيَاتِ رَبِّهِمْ إِلَّا كَانُوا عَنْهَا مُعْرِضِينَ
( 46 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 46 Ya-seen - Aya 46](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma wata ãyã daga ãyõyin Ubangijinsu bã ta zuwa a gare su, sai sun kasance sunã mãsu bijirẽwa daga gare ta.
وَإِذَا قِيلَ لَهُمْ أَنفِقُوا مِمَّا رَزَقَكُمُ اللَّهُ قَالَ الَّذِينَ كَفَرُوا لِلَّذِينَ آمَنُوا أَنُطْعِمُ مَن لَّوْ يَشَاءُ اللَّهُ أَطْعَمَهُ إِنْ أَنتُمْ إِلَّا فِي ضَلَالٍ مُّبِينٍ
( 47 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 47 Ya-seen - Aya 47](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma idan aka ce musu, "Ku ciyar daga abin da Allah Ya azurta ku," sai waɗanda suka kãfirta su ce ga waɗanda suka yi ĩmãni, "Ashe, zã mu ciyar da wanda idan Allah Ya so Yanã ciyar da shi? Ba ku zama ba fãce a cikin ɓata bayyananniya."
وَيَقُولُونَ مَتَىٰ هَٰذَا الْوَعْدُ إِن كُنتُمْ صَادِقِينَ
( 48 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 48 Ya-seen - Aya 48](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma sunã cẽwa, "A yaushe wannan wa'adi yake (aukuwa) idan kun kasance mãsu gaskiya?"
مَا يَنظُرُونَ إِلَّا صَيْحَةً وَاحِدَةً تَأْخُذُهُمْ وَهُمْ يَخِصِّمُونَ
( 49 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 49 Ya-seen - Aya 49](style/islamic/icons/mp3.png)
Bã su jiran (kõme) fãce wata tsãwa guda, zã ta kãma su, alhãli kuwa sunã yin husũma.
فَلَا يَسْتَطِيعُونَ تَوْصِيَةً وَلَا إِلَىٰ أَهْلِهِمْ يَرْجِعُونَ
( 50 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 50 Ya-seen - Aya 50](style/islamic/icons/mp3.png)
Bã zã su iya yin wasiyya ba, kuma bã zã su iya kõmãwa zuwa ga iyãlansu ba.
وَنُفِخَ فِي الصُّورِ فَإِذَا هُم مِّنَ الْأَجْدَاثِ إِلَىٰ رَبِّهِمْ يَنسِلُونَ
( 51 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 51 Ya-seen - Aya 51](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma aka yi bũsa a cikin ƙaho, to, sai gã su, daga kaburbura zuwa ga Ubangijinsu, sunã ta gudu.
قَالُوا يَا وَيْلَنَا مَن بَعَثَنَا مِن مَّرْقَدِنَا ۜ ۗ هَٰذَا مَا وَعَدَ الرَّحْمَٰنُ وَصَدَقَ الْمُرْسَلُونَ
( 52 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 52 Ya-seen - Aya 52](style/islamic/icons/mp3.png)
Suka ce: "Yã bonenmu! Wãne ne ya tãyar da mu daga barcinmu?" "Wannan shi ne abin da Mai rahama ya yi wa'adi da shi, kuma Manzanni sun yi gaskiya."
إِن كَانَتْ إِلَّا صَيْحَةً وَاحِدَةً فَإِذَا هُمْ جَمِيعٌ لَّدَيْنَا مُحْضَرُونَ
( 53 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 53 Ya-seen - Aya 53](style/islamic/icons/mp3.png)
Ba ta kasance ba fãce wata tsãwa ce guda, sai gã su duka, sunã abin halartarwa a gare Mu.
فَالْيَوْمَ لَا تُظْلَمُ نَفْسٌ شَيْئًا وَلَا تُجْزَوْنَ إِلَّا مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ
( 54 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 54 Ya-seen - Aya 54](style/islamic/icons/mp3.png)
To, a yau, bã zã a zãlunci wani rai da kõme ba. Kuma bã zã a sãkã muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
إِنَّ أَصْحَابَ الْجَنَّةِ الْيَوْمَ فِي شُغُلٍ فَاكِهُونَ
( 55 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 55 Ya-seen - Aya 55](style/islamic/icons/mp3.png)
Lalle, 'yan Aljanna, a yau, sunã cikin shagali, sunã mãsu nishãɗi.
هُمْ وَأَزْوَاجُهُمْ فِي ظِلَالٍ عَلَى الْأَرَائِكِ مُتَّكِئُونَ
( 56 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 56 Ya-seen - Aya 56](style/islamic/icons/mp3.png)
Sũ da mãtan aurensu sunã cikin inuwõwi, a kan karagai, sunã mãsu gincira.
لَهُمْ فِيهَا فَاكِهَةٌ وَلَهُم مَّا يَدَّعُونَ
( 57 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 57 Ya-seen - Aya 57](style/islamic/icons/mp3.png)
Sunã da, 'ya'yan itãcen marmari a cikinta kuma sunã sãmun abin da suke kiran a kãwo.
سَلَامٌ قَوْلًا مِّن رَّبٍّ رَّحِيمٍ
( 58 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 58 Ya-seen - Aya 58](style/islamic/icons/mp3.png)
"Aminci," da magana, daga Ubangiji Mai jin ƙai.
وَامْتَازُوا الْيَوْمَ أَيُّهَا الْمُجْرِمُونَ
( 59 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 59 Ya-seen - Aya 59](style/islamic/icons/mp3.png)
"Ku rarrabe dabam, a yau, yã kũ mãsu laifi!"
أَلَمْ أَعْهَدْ إِلَيْكُمْ يَا بَنِي آدَمَ أَن لَّا تَعْبُدُوا الشَّيْطَانَ ۖ إِنَّهُ لَكُمْ عَدُوٌّ مُّبِينٌ
( 60 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 60 Ya-seen - Aya 60](style/islamic/icons/mp3.png)
"Ashe, ban yi muku umurni na alkawari ba, yã ɗiyan Ãdamu? Cẽwa kada ku bauta wa Shaiɗan, lalle shĩ, maƙiyi ne a gareku bayyananne?"
وَأَنِ اعْبُدُونِي ۚ هَٰذَا صِرَاطٌ مُّسْتَقِيمٌ
( 61 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 61 Ya-seen - Aya 61](style/islamic/icons/mp3.png)
"Kuma ku bauta Mini. Wannan ita ce hanya madaidaciya."
وَلَقَدْ أَضَلَّ مِنكُمْ جِبِلًّا كَثِيرًا ۖ أَفَلَمْ تَكُونُوا تَعْقِلُونَ
( 62 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 62 Ya-seen - Aya 62](style/islamic/icons/mp3.png)
"Kuma lalle haƙĩƙa, (Shaiɗan) yã ɓatar da jama'a mãsu yawa daga gare ku. Ashe to ba ku kasance kunã yin hankali ba?"
هَٰذِهِ جَهَنَّمُ الَّتِي كُنتُمْ تُوعَدُونَ
( 63 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 63 Ya-seen - Aya 63](style/islamic/icons/mp3.png)
"Wannan ita ce Jahannama wadda kuka kasance anã yi muku wa'adi da ita."
اصْلَوْهَا الْيَوْمَ بِمَا كُنتُمْ تَكْفُرُونَ
( 64 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 64 Ya-seen - Aya 64](style/islamic/icons/mp3.png)
"Ku shigẽ ta a yau, sabõda abin da kuka kasance kunã yi na kãfirci."
الْيَوْمَ نَخْتِمُ عَلَىٰ أَفْوَاهِهِمْ وَتُكَلِّمُنَا أَيْدِيهِمْ وَتَشْهَدُ أَرْجُلُهُم بِمَا كَانُوا يَكْسِبُونَ
( 65 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 65 Ya-seen - Aya 65](style/islamic/icons/mp3.png)
A yau, Munã sanya hãtimin rufi a kan bãkunansu, kuma hannãyensu su yi Mana magana, kuma ƙafãfunsu su yi shaidu da abin da suka kasance sunã aikatãwa.
وَلَوْ نَشَاءُ لَطَمَسْنَا عَلَىٰ أَعْيُنِهِمْ فَاسْتَبَقُوا الصِّرَاطَ فَأَنَّىٰ يُبْصِرُونَ
( 66 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 66 Ya-seen - Aya 66](style/islamic/icons/mp3.png)
Dã Mun so, dã Mun shãfe gani daga idãnunsu, sai su yi tsẽre ga hanya, to, yaya zã su yi gani?
وَلَوْ نَشَاءُ لَمَسَخْنَاهُمْ عَلَىٰ مَكَانَتِهِمْ فَمَا اسْتَطَاعُوا مُضِيًّا وَلَا يَرْجِعُونَ
( 67 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 67 Ya-seen - Aya 67](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma da Mun so, da Mun juyar da halittarsu a kan halinsu, saboda haka ba zã su iya shuɗewa ba, kuma ba zã su komo ba.
وَمَن نُّعَمِّرْهُ نُنَكِّسْهُ فِي الْخَلْقِ ۖ أَفَلَا يَعْقِلُونَ
( 68 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 68 Ya-seen - Aya 68](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma wanda Muka rãya shi, Manã sunkuyar da shi ga halittarsa. Ashe, bã su hankalta?
وَمَا عَلَّمْنَاهُ الشِّعْرَ وَمَا يَنبَغِي لَهُ ۚ إِنْ هُوَ إِلَّا ذِكْرٌ وَقُرْآنٌ مُّبِينٌ
( 69 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 69 Ya-seen - Aya 69](style/islamic/icons/mp3.png)
Ba Mu sanar da shi (Annabi) wãkã ba, kuma wãkã ba ta kamãta da shi (Annabi) ba. Shi (Al-ƙur'ãni) bai zama ba fãce tunãtarwa ce, da abin karãtu bayyananne.
لِّيُنذِرَ مَن كَانَ حَيًّا وَيَحِقَّ الْقَوْلُ عَلَى الْكَافِرِينَ
( 70 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 70 Ya-seen - Aya 70](style/islamic/icons/mp3.png)
Dõmin ya yi gargaɗi ga wanda ya kasance mai rai, kuma magana ta wajaba a kan kãfirai.
أَوَلَمْ يَرَوْا أَنَّا خَلَقْنَا لَهُم مِّمَّا عَمِلَتْ أَيْدِينَا أَنْعَامًا فَهُمْ لَهَا مَالِكُونَ
( 71 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 71 Ya-seen - Aya 71](style/islamic/icons/mp3.png)
Shin, ba su gani ba (cẽwa) lalle Mun halitta musu dabbõbi daga abin da HannayenMu suka aikata, sai sunã mallakar su?
وَذَلَّلْنَاهَا لَهُمْ فَمِنْهَا رَكُوبُهُمْ وَمِنْهَا يَأْكُلُونَ
( 72 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 72 Ya-seen - Aya 72](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma Muka hõre su, sabõda su, sabõda haka daga gare su abin hawansu yake, kuma daga gare su suke ci.
وَلَهُمْ فِيهَا مَنَافِعُ وَمَشَارِبُ ۖ أَفَلَا يَشْكُرُونَ
( 73 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 73 Ya-seen - Aya 73](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma sunã da waɗansu amfãnõni a cikinsu, da abũbuwan shã. Ashe fa, bã zã; su gõdẽ ba?
وَاتَّخَذُوا مِن دُونِ اللَّهِ آلِهَةً لَّعَلَّهُمْ يُنصَرُونَ
( 74 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 74 Ya-seen - Aya 74](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma suka riƙi waɗansu abũbuwan bautãwa wanin Allah, ɗammãninsu zã su taimake su.
لَا يَسْتَطِيعُونَ نَصْرَهُمْ وَهُمْ لَهُمْ جُندٌ مُّحْضَرُونَ
( 75 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 75 Ya-seen - Aya 75](style/islamic/icons/mp3.png)
Bã zã su iya taimakonsu ba, alhãli kuwa sũ runduna ce wadda ake halartarwa (a cikin wutã).
فَلَا يَحْزُنكَ قَوْلُهُمْ ۘ إِنَّا نَعْلَمُ مَا يُسِرُّونَ وَمَا يُعْلِنُونَ
( 76 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 76 Ya-seen - Aya 76](style/islamic/icons/mp3.png)
Sabõda haka, kada maganarsu ta ɓãta maka rai. Lalle Mũ, Munã sanin abin da suke asirtãwa da abin da suke bayyanãwa.
أَوَلَمْ يَرَ الْإِنسَانُ أَنَّا خَلَقْنَاهُ مِن نُّطْفَةٍ فَإِذَا هُوَ خَصِيمٌ مُّبِينٌ
( 77 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 77 Ya-seen - Aya 77](style/islamic/icons/mp3.png)
Ashe, kuma mutum bai ga (cẽwa) lalle Mũ, Mun halitta shi daga maniyyi ba, sai gã shi mai yawan husũma, mai bayyanãwar husũmar.
وَضَرَبَ لَنَا مَثَلًا وَنَسِيَ خَلْقَهُ ۖ قَالَ مَن يُحْيِي الْعِظَامَ وَهِيَ رَمِيمٌ
( 78 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 78 Ya-seen - Aya 78](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma ya buga Mana wani misãli, kuma ya manta da halittarsa, ya ce: "Wãne ne ke rãyar da ƙasũsuwa alhãli kuwa sunã rududdugaggu?"
قُلْ يُحْيِيهَا الَّذِي أَنشَأَهَا أَوَّلَ مَرَّةٍ ۖ وَهُوَ بِكُلِّ خَلْقٍ عَلِيمٌ
( 79 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 79 Ya-seen - Aya 79](style/islamic/icons/mp3.png)
Ka ce: "Wanda ya ƙãga halittarsu a farkon lõkaci Shĩ ke rãyar da su, kuma Shi, game da kõwace halitta, Mai ilmi ne."
الَّذِي جَعَلَ لَكُم مِّنَ الشَّجَرِ الْأَخْضَرِ نَارًا فَإِذَا أَنتُم مِّنْهُ تُوقِدُونَ
( 80 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 80 Ya-seen - Aya 80](style/islamic/icons/mp3.png)
"Wanda ya sanya muku wutã daga itãce kõre, sai gã ku kunã kunnãwa daga gare shi."
أَوَلَيْسَ الَّذِي خَلَقَ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضَ بِقَادِرٍ عَلَىٰ أَن يَخْلُقَ مِثْلَهُم ۚ بَلَىٰ وَهُوَ الْخَلَّاقُ الْعَلِيمُ
( 81 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 81 Ya-seen - Aya 81](style/islamic/icons/mp3.png)
"Shin, kuma Wanda Ya halitta sammai da ƙasã bai zama Mai ĩkon yi ba ga Ya halitta kwatankwacinsu? Na'am, zai iya! Kuma Shĩ Mai yawan halittãwa ne, Mai ilmi."
إِنَّمَا أَمْرُهُ إِذَا أَرَادَ شَيْئًا أَن يَقُولَ لَهُ كُن فَيَكُونُ
( 82 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 82 Ya-seen - Aya 82](style/islamic/icons/mp3.png)
UmurninSa idan Yã yi nufin wani abu sai Ya ce masa kawai, "Ka kasance," sai yana kasancewa (kamar yadda Yake nufi).
فَسُبْحَانَ الَّذِي بِيَدِهِ مَلَكُوتُ كُلِّ شَيْءٍ وَإِلَيْهِ تُرْجَعُونَ
( 83 ) ![Hausa - Ya-seen - Aya 83 Ya-seen - Aya 83](style/islamic/icons/mp3.png)
Sabõda haka, tsarki yã tabbata ga Wanda mallakar kõwane abu take ga HannãyenSa, kuma zuwa gare Shi ake mayar da ku.